Ƙungiyar makarantun islamiyya a jihar Kano sun bayyana ƙorafinsu akan yadda gwamnatin jihar Kano ta buɗe gidajen kallon bal a faɗin jihar inda kuma ta bar makarantun islamiyya a garƙame.
Wannan ƙorafi ya fito ne daga bakin wasu daga cikin shugabannin Islamiyya Aisha Ibrahim Ɗorayi da kuma Malam Hassan, a lokacin da su ke tattunawa da filin inda ranka da ake gabatarwa a tashar Freedom Radio da ke Kano.
Malaman makarantun Islamiyya sun ce za su yi zanga-zangar lumana ganin yadda gwamnati ta bude gidan kallo amma bata bude makarantun Islamiyya ba.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
- Tsohon sakataren jam’iyyar PDP na kasa ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC
Wannan dai yana zuwa ne kwanaki uku da gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da umarnin buɗe gidajen kallon ball da ke jihar Kano.
Gwamna Ganduje ya bayar da wannan umarnin ne a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar gidajen kallo a jihar Kano.
Hakazalika gwamnan ya yi kira ga masu gidan kallon su tabbatar da cewa an baiwa juna tazara a gidajen kallonsu.
A ƙarshe gwamna Ganduje ya ba su gudunmuwar takunkumin rufe baki guda 40,000 saboda suyi amfani da su wajen kalle-kallensu.