An kafa jam’iyyar Labour ne domin bunkasa muradun ma’aikata da ‘yan fansho – Ayuba Wabba

0 101

Tsohon shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya, Ayuba Wabba ya ce an kafa jam’iyyar Labour ne domin bunkasa muradun ma’aikata da ‘yan fansho na Najeriya.

Wabba ya bayyana haka ne a wata hira da gidan talabijin na Channels a jiya Alhamis.

A cewarsa, kungiyar kwadago ta NLC ce ta kafa jam’iyyar Labour a matsayin wata kafa da ya’yan kungiyar da za su yi amfani da ita wajen kare hakkinsu. Yace Wannan ya sabawa ikirarin da shugaban jam’iyyar ta Labour Julius Abure ya yi na cewa jam’iyyar ba ta da wata alaka da kungiyar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: