Bayan ikirarin da Gwamnatin tarayya tayi cewa farashin man fetur a kasar nan na daga cikin mafiya sauki a nahiyar Africa, kungiyar kwadago ta kasa hadi da wasu kungiyoyin fararen hula, sun bayyana hujjar da gwamnatin ta rika a matsayin maras tushe.
A wata hira da yan jaridu, Shugaban kungiyar na kasa Ayuba Wabba, yace kamata yayi gwamnatin ta alakanta karin farashin man da saukar darajar Naira, da kuma tsarin albashi mafi kankanta da ake biyan ma’aikata.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
Suma dai wasu rassan kungiyar na jihohi sunce karin farashin man da na kudin wuta, ya sanya sabon tsarin albashi mafi karanci na naira dubu 30 a matsayin anyi ba ayi ba.
A ranar litinin din da ta gabata ne dai ministan yada labarai da raya al’adu Lai Muhammad yace duk da karin kudin man da akayi, farashin kayan masarufi a kasarnan kawo yanzu, na daga cikin mafiya rangwami a fadin Africa.