

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin jihar Jigawa ta aike da sakon taaziyya da kuma jaje ga wadanda suka Mutu da kuma Jikata sanadiyyar rikicin Fulani da Manoma a karamar Hukumar Guri.
Mataimakin Gwamnan jiha Mallam Umar Namadi ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyarar jajen fadar mai martaba sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje a madadin gwamnan jiha Muhammad Badaru Abubakar.
Yace gwamnan ya nuna alhini dangane da abin da ya faru tare da bada tabbacin gwamnatin jiha na gudanar da bincike domin kawo karshen rikicin Fulani makiyaya da manoma a yankin Guri da ma kasa baki daya.
Mallam Umar Namadi ya ce gwamnati zata gudanar da bincike domin gano musabbabin rikicin da kuma daukar matakan da suka dace.
Inda suka bukaci Fulani makiyaya da manoma dasu cigaba da zama lafiya da junansu, yana mai cewar babu wani cigaba da za a samu muddin babu zaman lafiya.