Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta cafke wani mutum da ke kera Bam-bamai ga kungiyar IPOB

0 119

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta cafke wani da ake zargin dan asalin kungiyayar dake fafutikar kafa kasar Biafra ne ta IPOB bisa zargin cewa yana kera Bam-bamai a wani samame da suka kai a Uba Umuaka da ke karamar hukumar Njaba a jihar Imo.

An kama wanda ake zargin ne mai shekaru 50, Simeon Onigbo ne ranar Alhamis.

Da yake tabbatar da kamun a yau, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar CSP Michael Abattam, ya ce wanda ake zargin da aka yi masa tambayoyi a nan take, ya amince da cewa shi ne ya kera yawancin na’urori masu fashewa da ake amfani da su wajen kai hari ga ofisoshin ‘yan sanda a jihar da kuma wajen jihar.

Ya kuma ce Sashen Kashe Bama-Bamai na Rundunar, sun karbe bam din da aka gano domin tantancewa da kuma yiwuwar tayar da su.

Leave a Reply

%d bloggers like this: