

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
1- Bayan Fitowar sabbin bayanai Jihar Jigawa yanzu na da masu ɗauke da Korona 9
2- Mutum na farko a jihar ya rasu a dalilin cutar
3- Kwamishinan Lafiya kuma shuganan kwamitin ko ta kwana kan yaki da cutar na Jihar Dr Abba Zakari ne ya sanar da hakan a babban birnin jihar Dutse, a wani taron manema Labarai jiya
4- Sabbin ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗar da;

Dutse
Gwaram
Miga
Auyo
Birnin Kudu
Gumel
Gujungu a ƙaramar hukumar Taura
Duk za a kulle ranar Juma’a da karfe 12:00am (Dare) Kazaure na cikin lissafi
5- Gwajin waɗanda ake zargin na da cutar har yanzu babban kalubale ne a jihar Jigawa saboda babu wurin gwaji sai an je Kano ko Abuja, amma ana duba yiwuwar fara tuntubar asibitoci masu zaman kansu da hukumar NCDC ta tantance
6-Kamishinan lafiyar ya ce gwamnatin Jigawa zata fara rabon kayan abinci don rage raɗaɗin halin da ake ciki
7- Sai dai an samu bambancin lissafi idan aka kwatanta da alƙaluman da hukumar NCDC ta bayyana na masu ɗauke da cutar, hukumar a daren jiya ta ce, tana da labarin mutane 7 ne kacal dake da cutar a Jigawa sabanin 19 da gwamnatin jihar ta sanar (Duba cikin hoton ƙasan labarin)
