Shugaba Buhari yayi amannar cewa tsarin ‘yansandan jihoshi ba shi zai haifar da da mai ido ba ga Najeriya ba
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2021/12/Buhari-36.jpg?resize=612%2C408&ssl=1)
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari yayi amannar cewa tsarin ‘yansandan jihoshi ba shi zai haifar da da mai ido ba ga kasarnan.
Shugaban kasar ya sanar da haka a wata fira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, wacce ake haskawa a halin yanzu.
Shugaban kasar ya kare matsayarsa da cewa akwai yiwuwar gwamnoni suyi amfani da yansandan jihoshi wajen cimma burinsu na siyasa.
Da yake magana akan yanayin tsaro a kasarnan, shugaban kasar yace dole sarakunan gargajiya su taka muhimmiyar rawa wajen samun zaman lafiya a kauyukansu.
Ya kuma bukaci karin tattaunawa wajen magance rikicin manoma da makiyaya da ake samu a kasarnan.
A wani batun kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya nada Sanata Magaret Chuba Okadigbo a matsayin shugabar kwamitin gudanarwar kamfanin man fetur na kasa (NNPC).
Magaret Okadigbo ta maye gurbin Ifeanyi Ararume, wanda shugaban kasar ya nada lokacin da aka kaddamar da kwamitin a ranar 19 ga watan Satumbar bara.