Shugabannin jam’iyyun adawa na ADC da NNPP sun bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa ta fara sabon yunkuri na gyaran Dokar Zabe.
Da yake magana a madadin bangaren adawa a taron manema labarai da aka gudanar a Abuja, Shugaban NNPP na kasa, Ajuji Ahmed, ya nemi a cire duk wasu tanade-tanade da suke ganin ba su dace ba a dokar.
Ya bayyana cewa sabuwar Dokar Zabe ta 2026, wadda aka amince da ita kuma Bola Tinubu ya sanya wa hannu a ranar 18 ga Fabrairu, ta takaita hanyoyin fitar da ‘yan takara zuwa zabin kai tsaye ko tsarin maslaha kawai.
A cewarsa, dokar ta kuma rage tsawon lokacin yakin neman zabe da na gudanar da zaben fidda gwani, tare da tanadin cewa za a saki kudaden hukumar zabe INEC watanni shida kafin zabe maimakon watanni goma sha biyu kamar yadda aka saba.
Ahmed ya ce shugabannin adawa na kallon wasu sassa na dokar a matsayin yunkurin rage gaskiya da amincin zabe gabanin babban zaben 2027.
Ya soki tanadin Sashe na 60(3) wanda ya bai wa jami’in zabe ikon da ba a fayyace ba kan yada sakamakon zabe, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga isar da sakamako ta hanyar na’ura.
Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa ciki har da Atiku Abubakar, Peter Obi da David Mark, inda suka bukaci Majalisar Dokoki ta sake duba dokar domin tabbatar da zabe mai gaskiya da adalci wanda zai wakilci muradin al’ummar Najeriya.