Sojojin Isra’ila sun kai wani samame a cikin zirin Gaza

0 189

Sojojin Isra’ila da ke samun goyon bayan jiragen yaki sun kai wani samame a cikin zirin Gaza, in ji rundunar a yau Juma’a, yayin da take shirin kai farmaki ta kasa kan Hamas, domin kai hari mafi muni a tarihin kasar.

Yayin da rikicin ya barke a cikin kwanaki na 21, babu ja da baya a hare-haren da Isra’ila ke kai wa zirin Gaza ba tare da bata lokaci ba, inda shugabannin kasashen Turai suka yi kira da a dakatar da ayyukan jin kai don ba da damar kai agajin da ake bukata.

Isra’ila dai na kai hare-hare a yankin Falasdinawa tun bayan da ‘yan Hamas suka kai farmaki kan iyakar kasar a ranar 7 ga watan Oktoba, inda suka kashe mutane 1,400 galibi fararen hula tare da yin garkuwa da wasu fiye da 220 a cewar jami’an Isra’ila.

Ya zuwa yanzu, ma’aikatar lafiya ta Hamas ta Gaza ta ce hare-haren sun kashe mutane sama da 7,000, galibi fararen hula da yawancinsu kananan yara ne, lamarin da ke kara yin kira da a kare mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, wadanda rikicin ya rutsa da su. Yayin da dubun-dubatar sojojin Isra’ila suka yi dafifi a iyakar Gaza gabanin wani farmakin da ake kyautata zaton kai wa a kasa, rundunar ta ce dakarunta sun yi wani dan takaitaccen kutse a tsakiyar Gaza.

Leave a Reply

%d bloggers like this: