Wani babban jirgin yakin Najeriya ya fado a Kaduna inda matukin jirgin ya mutu

0 48

Mun sami wani rahoto da ke cewa wani jirgin yaki mallakin rundunar sojojin sama na Najeriya ya yi fado a jihar Kaduna.

A halin yanzu ba mu sami cikakken bayani ba, amma wata majiya na cewa matukin jirgin ya rasa ransa a sanadin hadarin.

Hadarin ya auku kasa da shekara guda bayan da wasu manyan hafsoshin sojin kasar, ciki har da Janar Ibrahim Attahiru – wanda shi ne hafsan sojojin kasa na kasar – suka halaka.

Leave a Reply

%d bloggers like this: