Jami’an yan sanda a jihar Kaduna sun kama sama da mutane 217 wadanda aka amince cewa sune da alhakin kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma fashi da makami a jihar.
Cikin wannan makon yan bindiga sun kashe tare da sace mutane da yawa a wasu yankuna da ke jihar.
Kwamishinan yan sandan jihar Umar Muri wanda ya mika wadanda ake zargi ga helikwantar rundunar a kaduna a jiya laraba, ya kuma nuna bindigogi da suka hada AK47 da sauran makamai da aka kwato daga wajan yan bindigar.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Umar Muri ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin tsakanin ranar 29 ga watan afrailu zuwa 22 ga watan yunin wannan shekarar.
Ya kara da cewa haka kuma rundunar ta kwato milyoyin jabin kudade na kasashen ketare da na gida, da kuma buhuhunan shinkafa, motoci, babura, talabijin, wayoyin tarho, kamfuyutoci, shanaye, jabin ID cards na yan sanda, da kuma tabar wiwi daga hannun wadanda ake zargin.