Sashen bada horo da jagoranci dake ofishin shugaban ma’aikata na jihar Jigawa yace a gobe Asabar 10 ga wata ne za a kai matasan jihar Jigawa zuwa makarantar horas da kananan hafsoshin soji ta NDA dake Kaduna domin ganawa dasu.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
A sanarwar da Daraktan sashen Ibrahim Abdullahi ya bayar ta bukaci matasan da za a gana da su da su hallara a ofishin hukumar bada guraben karatu ta jiha dake Dutse da misalin karfe 7 na safe domin dibarsu zuwa Kaduna.
Sanarwar ta bukaci matasan da abin ya shafa da su kiyaye da wannan sanarwa kuma su zo akan lokaci.