

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya sanar da amincewa da karin kashi 30% na albashin likitoci a kananan hukumomi bakwai da ke jihar.
Zulum Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar da ya kai da daddare a babban asibitin Monguno a ranar Asabar.
Baya ga likitoci, ma’aikatan jinya, ungozoma, kwararrun dakin gwaje-gwaje, likitoci da sauran ma’aikatan lafiya na kananan hukumomin bakwai za su ci gajiyar karin kashi 20% na albashi da nufin zaburar da su wajen gudanar da ayyukan kiwon lafiya masu inganci da araha.
Kananan hukumomi bakwai sun hada da, Monguno, Ngala, Dikwa, Kukawa, Kala-Balge Abadam da kuma Banki.
Gwamnan ya kuma ba da umarnin gina karin rukunin ma’aikata da samar da rijiyoyin burtsatse masu zurfi da kuma hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana don inganta ayyuka a wurin.