An sace Sarki mai daraja ta 2 da karin wasu mutane 20

0 143

A wani labarin makamancin wannan, Wasu ‘Ya bindiga akae kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun sace Sarki mai daraja ta 2 da karin wasu mutane 20 a Yankin Pupule  a karamar hukumar Yorro dake Jihar Taraba.

‘Yan bindigar sun mamaye yankin ne da misalin 2 na dare inda suka sace mutane 21 a garin.

Majiyoyi daga garin,sunce ‘Yan bindigar  sun sace Sarkin Mai Daraja ta 2 Umaru Abubakar, da D’an sa da kuma matar sa mai juna biyu. Kakakin ‘Yan sandan Jihar Usman Abdullahi shima ya tabbatar da faruwar lamarin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: