Gwamna Nasiru El-Rufa’i na jihar Kaduna yace bangaren shari’a a jihar bazai sake bayar da belin masu fyade ba, daidai lokacin da ake duba yiwuwar dandake wadanda aka yankewa hukuncin fyade.
El-Rufa’i ya sanar da haka lokacin da wata tawagar mata da ke neman adalchi ga wadanda ake yiwa fyade, ta shirya wata zanga-zangar lumana a gidan gwamnati dake Kaduna a jiya.
Yace alkalin alakai na jihar ya bayar da tabbacin cewa daga yanzu baza a sake bayar da belin duk wanda aka zarga da aikata fyade ba, ta kowane hali, kasancewar suna komawa su sake aikata laifin.
- NEMA ta tarbi ƴan Najeriya 147 da aka dawo da su daga Nijar
- Najeriya za ta kwashe mutanenta daga Isra’ila da Iran
- INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP
- Gwamnatin Jigawa ta ware naira biliyan 2 domin gina magudanan Ruwa da Gadaje
- Najeriya ta shigo da danyen man fetur na sama da naira tiriliyan 1.19 a cikin watanni uku
A cewarsa, tuni jihar take da tsatstsauran hukunci akan laifin aikata fyade.
Sai dai, El-Rufa’i yace gwamnati na duba yiwuwar gyaran dokar domin sanya dandaka ga duk wanda aka zartarwa da hukuncin fyade.
A cewarsa, tuni wani dan majalisar dokokin jihar ya shirya gabatar da kudiri akan sanya dandaka.