Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, a jiya ya kaddamar da wasu kwamitoci guda biyu da zasu tabbatar da komawar yan gudun hijira zuwa kananan hukumomin jihar da aka yanto.
Tuni gwamnati a watan da ya gabata ta fara aikin mayar da yan gudun hijiran daga babban birnin jihar, Maiduguri, da sauran kananan hukumomi, zuwa garuruwansu na ainihi.
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
- Mutum takwas sun mutu a hatsarin mota a jihar Kogi
- An sallami wasu sojoji daga aiki bisa yin wata gagarumar sata a matatar manfetur ta Dangote
- Najeriya ba ta kaimatakin da za’a kirkiri ‘yan sandan jihohi ba – Kayode Egbetokun
- Gwamnatin tarayya na sa ran karɓar rancen dala biliyan 2.2 daga bankin duniya
Rikicin da ake cigaba da yi a Arewa maso Gabas kawo yanzu ya raba mutane miliyan 2 da dubu 700 da gidajensu, a cewar wani rahoton hukumar kula da yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya.
Daga cikin wannan adadin, kimanin kashi 80 cikin 100 sun fito ne daga jihar Borno, inda nan ne jihar da rikicin na sama da shekaru 10 yafi kamari.
Jihar Borno tana da sansanonin yan gudun hijira na gwamnati guda 32, da wasu wadanda bana gwamnati ba, wanda ba san adadinsu ba, kuma suke dauke da mafiya yawan yan gudun hijira.