

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC tace zata shigo da tsarin dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa a zabukan da ba na gama gari ba, farawa daga shekara mai zuwa.
Wannan na kunshe ne cikin kunshin dokokin hukumar mai shafuka 17 akan gudanar da zabuka lokacin annobar corona, dauke da sa hannun shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, da aka rabawa manema labarai a Abuja.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Sai dai, hukumar tace ba za a dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa ba a zabukan gwamnonin dake gabatowa a jihoshin Edo da Ondo.
Hukumar tace za tayi amfani da shafukan na’ura mai kwakwalwa wajen mika takardun neman shiga zabe daga jam’iyyun siyasa domin zabukan gwamnonin biyu.

Hukumar ta INEC tace lokacin zabukan Edo da Ondo, wadanda aka shirya yi a ranakun 19 ga watan Satumbar bana da 10 ga watan Oktoban bana,sanya takunkumin rufe fuska zai zaman tilas ga masu jefa kuri’a, da jami’an zabe da duk wanda ya halarci guraren zabe.