Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC tace zata shigo da tsarin dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa a zabukan da ba na gama gari ba, farawa daga shekara mai zuwa.
Wannan na kunshe ne cikin kunshin dokokin hukumar mai shafuka 17 akan gudanar da zabuka lokacin annobar corona, dauke da sa hannun shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, da aka rabawa manema labarai a Abuja.
- Kananun yara 5 ne suka mutu sakamakon rashin iska a cikin motar da suka makale a jihar Neja
- Yan sanda a Jihar Kaduna sun kama wani babban mai sayar wa ’yan bindiga makamai
- ‘Yan bindiga da ke addabar al’umma sun ajiye makamansu bayan wata tattaunawar sulhu
- Bobrisky ya ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin kotun da ta aike dashi gidan gyaran hali
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
Sai dai, hukumar tace ba za a dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa ba a zabukan gwamnonin dake gabatowa a jihoshin Edo da Ondo.
Hukumar tace za tayi amfani da shafukan na’ura mai kwakwalwa wajen mika takardun neman shiga zabe daga jam’iyyun siyasa domin zabukan gwamnonin biyu.
Hukumar ta INEC tace lokacin zabukan Edo da Ondo, wadanda aka shirya yi a ranakun 19 ga watan Satumbar bana da 10 ga watan Oktoban bana,sanya takunkumin rufe fuska zai zaman tilas ga masu jefa kuri’a, da jami’an zabe da duk wanda ya halarci guraren zabe.