Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC tace zata shigo da tsarin dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa a zabukan da ba na gama gari ba, farawa daga shekara mai zuwa.
Wannan na kunshe ne cikin kunshin dokokin hukumar mai shafuka 17 akan gudanar da zabuka lokacin annobar corona, dauke da sa hannun shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, da aka rabawa manema labarai a Abuja.
- Jagoran juyin mulkin Gabon na yin kokarin kawo karshen takunkumin da aka kakabawa kasar
- Rikicin soyayya ya yi sandiyyar mutuwar wani matashi dan jami’a
- An kama wasu mutane 2 bisa zargin kisan wani mutum a jihar Filato
- Gwamnatin Najeriya na kokarin samar da ingantaccen tsarin kiwon lafiya ga ‘yan Najeriya
- Ana tuhumar mai dakin Ali Bongo da laifin karkatar da kudade da wasu laifuffuka
Sai dai, hukumar tace ba za a dangwala kuri’a ta na’ura mai kwakwalwa ba a zabukan gwamnonin dake gabatowa a jihoshin Edo da Ondo.
Hukumar tace za tayi amfani da shafukan na’ura mai kwakwalwa wajen mika takardun neman shiga zabe daga jam’iyyun siyasa domin zabukan gwamnonin biyu.

Hukumar ta INEC tace lokacin zabukan Edo da Ondo, wadanda aka shirya yi a ranakun 19 ga watan Satumbar bana da 10 ga watan Oktoban bana,sanya takunkumin rufe fuska zai zaman tilas ga masu jefa kuri’a, da jami’an zabe da duk wanda ya halarci guraren zabe.