

A wani labarin kuma, Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya tana tantance kamfanonin cikin gida 19 domin samar da maganin gargajiyan da zai magance cutar corona.
Kamfanonin sun yi ikirari daban-daban, wadanda suka hada da samar da maganin cutar corona kai tsaye zuwa samar da maganin da zai warkar da alamun cutar.
Kamfanonin sun gana da shugabannin ma’aikatar tare da sashen kula da magungunan gargajiya.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Sai dai, an bukaci kamfanonin da su gabatar da samfurin magungunansu zuwa ga hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC, daga cikinsu za a zabi kamfanoni 3 wadanda za a tallafawa da kudade.
Karamin ministan lafiya, Sanata Adeleke Mamora, shine ya tabbatar da hakan yayin zantawa da manema labarai.