A wani labarin kuma, Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya tana tantance kamfanonin cikin gida 19 domin samar da maganin gargajiyan da zai magance cutar corona.
Kamfanonin sun yi ikirari daban-daban, wadanda suka hada da samar da maganin cutar corona kai tsaye zuwa samar da maganin da zai warkar da alamun cutar.
Kamfanonin sun gana da shugabannin ma’aikatar tare da sashen kula da magungunan gargajiya.
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
- An dakatar da Daraktan kwalejin Birnin Kudu da jami’in kula da harkokin abinchi na kwalejin
Sai dai, an bukaci kamfanonin da su gabatar da samfurin magungunansu zuwa ga hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC, daga cikinsu za a zabi kamfanoni 3 wadanda za a tallafawa da kudade.
Karamin ministan lafiya, Sanata Adeleke Mamora, shine ya tabbatar da hakan yayin zantawa da manema labarai.