

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Bayan da jihohin Arewa suka cimma matsaya akan dakatar da al’amarin Almajirci a yankin, ta hanyar mayar da kowanne Almajiri garin da ya fito, yanzu haka jihar Jigawa ta karbi irin wadannan Almajirai da aka koro masu yawan gaske da suka doshi dubu. A hakan ma wasu na kan hanyar su ta zuwa.
Yanzu haka gwamnatin jihar Jigawa ta yi hayar wani kamfani dake Kaduna domin yiwa Almajiran da aka kwaso daga Kano gwajin cutar Korona kafin kyale su shiga cikin gari don komawa cikin iyalansu.
Almajiran da yanzu suke killace a sansanin masu yiwa ƙasa hidima (NYSC) a ƙaramar Hukumar Kiyawa.
Ƙarin wasu Almajiran 69 da aka debo daga Gombe za’a killace su har tsawon kwanaki goma kafin a gwada su.