

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Babban alkalin Jihar Katsina, Mai shari’a Musa Abubakar Danladi, ya bayar da umarnin sakin fursunoni 185 daga gidajan yarin da ke fadin jihar, wani bangare na dakile yaduwar cutar COVID19 wajan ragewa cunkosan jama’a.
Cikin sanarawar da bababan magatakardar jihar Katsina, Alhaji Kabir Shu’aibu ya sanyawa hannu kuma ya rabawa manema labarai a jihar katsina, yace sakin fursunonin ya biyo bayan umarnin cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta najeriya NCDC, da kuma shugaban alkalin alkalan Najeriya Muhammad Tanko.

A wani labarin kuma gwamnatin jihar ta Katsina ta fara bincike gida gida nay an jihar da suka dawo daga jihar legas ko Abuja ko kuma wasu jihohin da aka samu rahoton bullar cutar COVID19.
Shugaban kwamitin karta kwana kan cutar COVID19 a jihar katsina kuma kwamishinan yada labarai Alhaji Haddi Muhammad ya shine ya fitar da sanarwar hakan.