Gwamnatin Jihar Jigawa ta rabawa manoma 50 ingantaccen irin shuka dan Brazil domin nomawa a gona mai fadin kadada 80 a wannan damina.
Mai bawa Gwamna shawara kan noman shinkafa, Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawaga ta masu ruwa da tsaki a aikin gona zuwa wasu fadamu dake kananan hukumomin Dutse da Hadejia da Kazaure.
- Gwamna Otu Ya Fadi Abubuwan da ke Janye Gwamnoni zuwa jam’iyar APC
- Atiku Abubakar yayi magana kan ficewar sa daga PDP
- Hukumar NEMA ta karɓi ‘yan Najeriya 203 da aka kwaso daga kasar Libya
- Kwamiti na jam’iyyar PDP ta yanke shawarar daukar matakin shari’a kan Sheriff Oborevwori
- Hukumar NDLEA ta yi nasarar kama kwayoyin da kudinsu ya haura naira biliyan 2.6 a Jihar Jigawa
Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya shawarci manoman da aka rabawa irin, da su tabbatar sun cika alkawuran da suka dauka na dawo da rancen iri ko kudaden da aka basu domin wasu manoman su amfana.
A nasa jawabin, mukaddashin Manajan Daraktan hukumar bunkasa aikin gona da raya karkara ta jiha, JARDA, Alhaji Bashir Mu’azu Majiya ya yi kira ga manoman da su rika aiki da shawarwarin malaman gona domin bunkasa nomansu.