Gwamnatin Jihar Jigawa ta rabawa manoma 50 ingantaccen irin shuka dan Brazil domin nomawa a gona mai fadin kadada 80 a wannan damina.
Mai bawa Gwamna shawara kan noman shinkafa, Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawaga ta masu ruwa da tsaki a aikin gona zuwa wasu fadamu dake kananan hukumomin Dutse da Hadejia da Kazaure.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Alhaji Jamilu Dan-Mallam ya shawarci manoman da aka rabawa irin, da su tabbatar sun cika alkawuran da suka dauka na dawo da rancen iri ko kudaden da aka basu domin wasu manoman su amfana.
A nasa jawabin, mukaddashin Manajan Daraktan hukumar bunkasa aikin gona da raya karkara ta jiha, JARDA, Alhaji Bashir Mu’azu Majiya ya yi kira ga manoman da su rika aiki da shawarwarin malaman gona domin bunkasa nomansu.